Labarai | 23.01.2008 | 07:00 UTC
´Yan sanda sun awon gaba da jagoran ´yan adawa a Zimbabwe
A ƙasar Zimbabwe an kame shugaban ´yan adawa na ƙasar Morgan Tsivangirai kamar yadda lauyansa ya nunar. A cikin daren jiya ´yan sanda suka yi awon gaba da jagoran na ´yan adawa. A yau laraba jam´iyarsa ta Movement for Democratic Change ta shirya gudanar da zanga-zangar, domin ƙara matsawa shugaba Robert Mugabe lamba da a sake fasalin kundin tsarin mulkin ƙasar wanda zai tabbatar da kamanta adalci a zaɓen shugaban kasa da na ´yan majaliar dokoki da za a yi cikin watan Maris. ´Yan sanda sun haramta zanga-zangar saboda gudun yin artabu.
More briefs
Hare-haren Isra´ila a Zirin Gaza barazana ce ga zaman lafiya | 19.01.2008
Tashe-tashen hankula a Iraqi a ranar bukin Ashura | 19.01.2008
An sako Turawan nan uku da aka tsaresu a Kenya | 19.01.2008
´Yan sandan Pakistan sun cafke wani matashi bisa zargi kisan Bhutto | 19.01.2008
Shugaba Abbas ya baiyana matakin sojin Isra´ila a Gaza da cewa kisan kare dangi ne | 16.01.2008
Wani hari a Sri Lanka ya halaka mutane da yawa | 16.01.2008
Jam´iyar adawa a Kenya ta samu galaba a majalisar dokoki | 16.01.2008
Shugaban Amirka George Bush a Abu Dhabi. | 13.01.2008




