Labarai | 23.01.2008 | 07:00 UTC
Annan ya fara yin sulhu a rikicin siyasar Kenya
Tsohon babban sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Kofi Annan ya na Nairobin babban birni ƙasar Kenya don ganawa da shugaba Mwai Kibaki da jagoran ´yan adawa Raila Odinga. Jim kaɗan bayan isarsa a Nairobi mista Annan ya faɗawa manema labarai cewa zai nima mutanen biyu da su shiga tattaunawa kai tsaye kana kuma su girmama dokar ƙasa. Annan da sauran shugabannin Afirka dake ƙoƙarin yin sulhu suna fatan warware rikicin siyasar kasar da ya fara bayan zaɓen shugaban kasar da aka gudanar cikin watan Disamba, wanda Odinga da magoya bayansa suka yi zargin an tabƙa magudi.Kimanin mutane 700 aka kashe sannan aka tilastawa wasu dubu 250 barin gidajensu tun bayan bayyana sakamakon zaɓen na ranar 27 ga watan Disamba.
More briefs
´Yan sanda sun awon gaba da jagoran ´yan adawa a Zimbabwe | 23.01.2008
Hare-haren Isra´ila a Zirin Gaza barazana ce ga zaman lafiya | 19.01.2008
Tashe-tashen hankula a Iraqi a ranar bukin Ashura | 19.01.2008
An sako Turawan nan uku da aka tsaresu a Kenya | 19.01.2008
´Yan sandan Pakistan sun cafke wani matashi bisa zargi kisan Bhutto | 19.01.2008
Shugaba Abbas ya baiyana matakin sojin Isra´ila a Gaza da cewa kisan kare dangi ne | 16.01.2008
Wani hari a Sri Lanka ya halaka mutane da yawa | 16.01.2008
Jam´iyar adawa a Kenya ta samu galaba a majalisar dokoki | 16.01.2008






